in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rufe dandalin tattaunawa kan hakkin dan Adam na birnin Beijing karo na 7
2014-09-18 15:54:16 cri
An rufe dandalin tattaunawa na kwanaki biyu kan kare hakkin dan Adam na birnin Beijing karo na 7 a Alhamis din nan, taron da kungiyar manazarta kare hakkin dan Adam ta kasar Sin, da asusun kare hakkin dan Adam na kasar Sin suka dauki bakunci.

Yayin rufe taron na wannan karo mataimakin shugaban kungiyar manazarta hakkin dan Adam ta kasar Sin Ye Xiaowen, ya bayyana cewa dandalin tattaunawar ya mai da hankali kan sha'anin bunkasa harkar kare hakkin dan Adam na kasar Sin, kana mahalarta dandalin tattaunawar sun bayar da ra'ayoyinsu kan ma'anar kare hakkin dan Adam, da batun mu'amala tsakanin kasa da kasa a wannan fanni.

Sauran batutuwan da aka tattauna sun hada da kirkiro hanyoyin aiwatar da harkokin kasa, da tabbatar da hakkin dan Adam, da daidaita tsakanin ayyukan yaki da ta'addanci da kare hakkin dan Adam.

Kaza lika an samu kyakkyawan sakamako a zaman dandalin tattaunawar, matakin da zai taimaka wajen bunkasa sha'anin kare hakkin dan Adam na kasar Sin da ma a sauran sassan duniya baki daya.

Ban da wannan kuma, Ye Xiaowen ya kara da cewa, kasar Sin na fatan amfani da dandalin tattaunawar wajen yin mu'amala tare da sauran kasashe a wannan fanni, da sa kaimi ga sha'anin kare hakkin dan Adam na kasa da kasa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China