in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron tattaunawar hakkin dan Adam karo na 6 a nan birnin Beijing
2013-09-12 15:12:33 cri
A ranar alhamis 12 ga wata, a nan birnin Beijing, aka bude taron tattaunawa a kan hakkin dan Adam karo na 6 da za a shafe kwanaki 2 ana yin sa. Jami'an gwamnatoci da kwararru a fannin kare hakkin dan Adam da suka fito daga M.D.D. da sauran kasashe da yankuna 33 kimanin 100 suna halarta taron, inda za su tattauna sosai bisa batun samar da muhalli mai kyau wajen inganta hakkin dan Adam cikin dogon lokaci.

A cikin jawabin fatan alheri, da shugaban kwamitin raya hakkin dan Adam na kasar Sin Luo Haocai ya karanto, ya bayyana cewa, hakkin dan Adam ya shafi tattalin arziki, da siyasa, da zaman al'umma, da al'adu da dai sauransu, kafa wani tsari mai kyau don raya hakkin dan Adam, da kawo yanayin inganta hakkin dan Adamu cikin dogon lokaci muhimmin aiki ne wajen kare hakkin dan Adam.

A nasa jawabi shi ma, direktan ofishin kula da yada labaru na majalisar gudanarwa ta kasar Sin Cai Ming zhao ya ce, gwamnatin Sin ta mayar da girmama da kare hakkin dan Adam, a matsayin wata babbar ka'ida wajen mulkin kasar, kuma ta hada batun kare hakkin dan Adam da halin da kasar Sin ke ciki, don haka za a hada batun raya hakkin dan Adam, da batun raya tattalin arziki, da siyasa, da al'adu da zaman al'umma, da muhallin halittu tare, tana ta yin kokari wajen cimma burin samun bunkasuwa cikin dogon lokaci, ta hakan ne in ji shi za a raya batun kare hakkin dan Adam zuwa wani sabon matsayi.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China