in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala taron dandalin tataunawa kan hakkin dan Adam karo na 6 a birnin Beijing
2013-09-14 17:35:41 cri
Ran 13 ga wata da yamma, ne aka kammala taron dandalin tattaunawa kan batutuwan da suka shafi hakkin dan Adam karo na 6 a nan birnin Beijing, wanda aka shirya bisa hadin gwiwar cibiyar nazarin hakkin dan Adam ta kasar Sin, da asusun raya harkokin kare hakkin dan Adam na kasar Sin.

Yayin wannan taro mai taken "gina dauwamammen yanayin bunkasa harkokin kare hakkin dan Adam" an tattauna kan batuttuwan da dama, musamman batutuwa guda uku da suka hada da "doka da hakkin dan Adam", "gina zaman takewar al'umma da kare hakkin dan Adam", da kuma "tsaron yanki da kare hakkin dan Adam". A kwanaki biyu da suka gabata, wasu manyan jami'ai da masana kan hakkin dan Adam da suka halarci taron daga MDD, da kuma kasashe 33, da wakilan jakadun kasashen da abin ya shafa da ke nan kasar Sin, da wasu masanan hakkin dan Adam na kasar Sin kimanin 100, sun yi musayar ra'ayoyi kan batuttuwa daban daban a nan birnin Beijing. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China