in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na son ba da gudummawarta don shawo kan cutar Ebola cikin hanzari
2014-09-17 20:31:39 cri
Yau Laraba 17 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin, Hong Lei ya bayyana cewa, Sin na fatan ba da taimako wajen shawo kan cutar Ebola tare da sauran kasashen duniya cikin hanzari

Mr. Hong ya bayyana hakan a gun taron manema labaru, inda ya ce cewa, a kokarin kara nuna goyon baya ga wasu kasashen Afirka a fannin shawo kan cutar Ebola, da la'akari da bukatar gwamnatin Saliyo, da kuma amsa kiran kungiyar hukumar WHO na neman goyon baya kan yadda za a shawo kan cutar Ebola a Afirka, a jiya Talata 16 ga wata, gwamnatin Sin ta tura rukunin masu bincike daga cibiyar shawo kan cututtuka ta Sin mai kunshe da mutane 59 zuwa Saliyo, domin taimakawa kasar wajen yin bincike kan cutar Ebola, da zummar kara karfin Saliyo a fannin yin bincike. Wannan rukuni zai fara aiki a asibitin sada zumunci tsakanin Sin da Saliyo da Sin ta ba da taimako wajen kafa shi.

Ban da haka, mista Hong ya kara da cewa, Sin ta dade tanana ta kokarin shawo kan cutar Ebola tare da sauran kasashen duniya. Kuma ta ba da kayayyakin agaji ga kasashen Guinea, Liberiya, Saliyo, da kuma Guinea Bissau cikin sauri. Rukunonin likitoci da Sin ta tura zuwa kasashen waje sun aiwatara ci gaba da da ayyukansu yadda ya kamata duk da barazanar da suke fuskanta, baki daya likitoci 115 ne suka suke gudanar da ayyukan shawo kan cutar Ebola a wurin. A wannan karo, kasar ta Ssin ta kara tura ma'aikata 59, adadin dadon haka, yawan likitocin kasar Sin da ke wurin ya karu ya yanzu ya kai zuwa 174. Wannan ya bayyana dankon zumunci dake tsakanin Sin da kasashen Afirka, da kuma ra'ayin jin kai na jama'ar Sin.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China