in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 39 ne cutar Ebola ta hallaka a kasar Congo Kinshasa
2014-09-15 15:06:40 cri
Ministan ma'aikatar kiwon lafiya a kasar Congo Kinshasa Felix Kabange, ya ce yawan mutanen da suka rasa rayukansu a sakamakon kamuwa da cutar Ebola a kasar ya karu zuwa 39. Mr. Kabange ya kuma ce dukkanin wadannan mutane na zaune ne a jihar Equateur.

Ministan lafiyar ya kuma bayyana cewa, ya zuwa ranar Asabar din da ta gabata, akwai mutane 66 da ko dai an tabbatar, ko kuma ana zaton sun dauke da cutar ta Ebola a kasar, kuma tuni 39 cikin wannan adadi suka rasu, ciki hadda jami'an jinya su 8.

Har wa yau ya ce cikin mutane 626 da a baya aka killace, an sallami mutane 342, yayin da ake ci gaba da sa ido tare da killacewa ragowar mutane 284.

Wannan ne dai karo na 7 da aka samu bullar cutar Ebola a kasar Congo Kinshasa, ko da yake hakan ba shi da nasaba da yaduwar cutar a kasashen Guinea, da Saliyo da sauran wasu kasashen yankin yammacin Afirka. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China