in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD za ta kafa cibiyar dakile cutar Ebola
2014-09-06 16:19:56 cri
Babban magatakardan MDD mista Ban Ki-moon ya bayyana a Jumma'a 5 ga wata cewa, majalisarsa ta tsai da kudurin kafa cibiyar dakile cutar Ebola don daidaita ayyukan bangarori daban daban, ta yadda za a samu damar dakatar da bazuwar cutar cikin watanni 6 zuwa 9. Haka zalika, a nata bangare, kungiyar kasashen Turai EU ta sanar da cewa za ta samar tallafin kudi kimanin Euro miliyan 140 don yaki da annobar.

A ranar Jumma'a Ban Ki-moon ya yi taro tare da shugabanni da kwararru na hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO, da bankin duniya, da hukumar raya kasashe ta MDD, da dai sauran hukumomi. Mista Ban ya shaida wa manema labaru a bayan taron cewa, mahalartar taron sun yanke shawarar kafa cibiyar dakile cutar Ebola, don daidaita kokarin da sassa daban daban suke yi ta fuskar hana bazuwar cutar Ebola.

Ban da haka kuma, kwamitin kungiyar EU ya sanar a ranar Jumma'a da cewa, zai samar da tallafin kudin da yawansa ya kai kimanin Euro miliyan 140 don taimakawa kasashen Guinea, Saliyo, Laberiya, da Najeriya wajen yakar cutar Ebola. Haka kuma, an ce za a kasa kudin zuwa kashi guda 3 don kyautata fasahar aikin jinya, da horar da ma'aikatan jinya, gami da tallafawa kasashen Laberiya da Saliyo, wadanda suka fi gamuwa da matsala a fannin kasafin kudi. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China