Wani mai magana da yawun MDDr ya shaidawa 'yan jaridu cewa ya zuwa yanzu akwai ma'aikatan tawagar wanzar da zaman lafiya fiye da 70 da aka kubutar, suke kuma wani wuri mai samun kariyar jami'an tsaro.
A ranar Asabar ne dai wata tawagar MDD mai kunshe da dakarun musamman ta UNDOF ta samu nasarar kubutar da wasu ma'aikatan su 32, an kuma ce jami'an sun samu kubuta ba tare da samun koda kwarzane ba.
Sai dai a daya hannun, kakakin MDDr ya ce har ya zuwa yanzu akwai wasu ma'aikatan wanzar da zaman lafiyar MDDr su 44, dake hannun mayaka 'yan gwagwarmayar kasar Sham.(Saminu Alhassan)