in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ofishin MDD ya yi Allah wadai da ci gaba da musayar wuta a Tripoli
2014-08-13 10:59:39 cri
Ofishin tawagar MDD mai kula da ayyukan wanzar da zaman lafiya a kasar Libiya ko UNSMIL a takaice, ya bayyana takaicin sa game da yadda mayakan kungiyoyin kasar ke ci gaba da musayar wuta a birnin Tripoli.

A cewar kakakin ofishin, lokaci ya yi da daukacin sassan da basa ga maciji da juna za su koma teburin shawara, karkashin shirin UNSMIL na shiga tsakani.

Kaza lika ofishin tawagar ta wanzar da zaman lafiya ya yi kira ga bangarorin dake adawa da juna, da su kauracewa amfani da karfi wajen warware banbancin ra'ayin siyasa dake tsakanin su.

Kakakin ofishin ya kuma bayyana damuwa kwarai, game da halin karacin kayayyakin kula da lafiya da ake fuskanta, da lalacewar ababen more rayuwa, tare da matsalar rasa matsuguni da dubban al'ummar kasar ke fuskanta.

Kaza lika ya bayyana damuwar ofishin sa, game da ci gaban rikici a sassan gabashin kasar, tare da hare-haren da ake kaiwa kan ofisoshin 'yan sanda da na soji, da ma amfani da jiragen saman yaki wajen kaddamar da irin wadannan hare-hare.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China