in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a dora muhimmanci game da yin shawarwari kan bunkasuwar tattalin arziki tare da Sin, in ji shugaban Zimbabwe
2014-08-23 16:03:01 cri
Bisa goron gayyatar shugaban kasar Sin Xi Jinping, daga ranar 24 zuwa 28 ga wata, shugaban Zimbabwe Robert Mugabe zai kawo ziyarar aiki a kasar Sin. Kafin zuwansa kuma, yayin da yake magana da 'yan jaridar kasar Sin, shugaba Mugabe, mai shekaru 90 a duniya ya bayyana cewa, ba ma kawai Zimbabwe da Sin na da dankon zumunci a tsakaninsu ba, har ma za su yi kokari tare domin bunkasa tattalin arziki. A sabili da haka, ziyarar da zan zai kai a Sin a wannan karo ta fi na da muhimmanci sosai.

Shugaba Mugabe ya ce, dangantaka tsakanin kasashen biyu na da dogon tarihi. Yayin da jama'ar Zimbabwe suke gwagwarmaya domin samun 'yancin kai, Sin ta ba da gudummawa sosai. 'Ba za a manta da wannan taimako ba, kuma ba za a manta cewa jama'ar Sin aminanmu ne ba a duniya', a cewar shugaban..

Yayin da jama'ar Zimbabwe suke gwagwarmaya wajen yaki da 'yan mulkin mallaka bisa jagorancinsa a shekarar 1977, Robert Mugabe ya taba kawo ziyara a Sin. Tun bayan da ya dauki mulkin kasarsa, ya taba kawo ziyara a Sin sama da sau 10, har ma ya kasance daya daga cikin shugabannin kasashen Afirka da suka fi kawo ziyara a kasar Sin. A sabili da haka, an rada masa suna 'abokin Sinawa da aka fi samun fahimta'. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China