in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Guo Jinlong ya gana da shugaban kasar Zimbabwe
2014-07-17 10:50:09 cri

Mamba a hukumar harkokin siyasa ta kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, kuma daraktan kwamitin jam'iyyar kwaminis na birnin Beijing Guo Jinlong, ya gana da shugaban kasar Zimbabwe kuma shugaban jam'iyyar ZANU-PF ta kasar Robert Mugabe a birnin Harare.

A yayin ganawar da suka yi a jiya Laraba, Guo Jinlong ya yabawa shugaba Mugabe, da kasancewarsa jagora dake matukar kokarin kasarsa ta samu cikakken 'yanci a nahiyar Afirka, baya ga gudummawar da ya bayar wajen samun 'yancin kai da ci gaba a nahiyar Afirka, da raya dangantakar dake tsakanin kasarsa da kasar Sin, da ma dangantakar daukacin kasashen Afirka da kasar ta Sin.

Mr. Guo ya ce bayan kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin kasarsa da Zimbabwe, yanzu hakan ana inganta wannan dangantaka yadda ya kamata. Kuma kasar Sin za ta ci gaba da bi ka'idojin sada zumunta da na hadin gwiwa, wajen raya dangantakar aminci a tsakaninta da kasashen Afirka, ciki har da kasar Zimbabwe, bisa manufar hadin gwiwar Sin da Afirka da firaministan Sin Li Keqiang ya gabatarwa kungiyar AU a bana.

A nasa bangare, shugaba Mugabe ya bayyana cewa, kasarsa na godiya ga irin taimako da Sin ke ba ta wajen inganta tattalin arziki, da zamantakewar al'umma, da kuma goyon baya gare ta kan harkokin kasa da kasa. Ya ce, Zimbabwe na dora muhimmanci kwarai ga raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin, da kuma dangantakar jam'iyyun kasashen biyu. Daga nan sai ya yi fatan kasashen biyu za su kara yin hadin gwiwa a fannonin aikin gona, da ayyukan more rayuwa, da sashen makamashi da dai sauransu, a kokarin daga darajar dangantakar sassan biyu zuwa wani sabon matsayi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China