in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi maraba da ci gaban da aka samu a aikin lalata makamai masu guba na kasar Syria
2014-08-21 16:04:35 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya bayar da wata sanarwa ta hannun kakakinsa a ranar 20 ga wata, inda ya yi maraba da rokon da kasar Syria ta gabatar na lalata makamanta masu guba a jirgin ruwan soja na kasar Amurka mai suna Cape Ray.

Sanarwar ta bayyana cewa, wannan wani babban ci gaba ne a aikin lalata makamai masu guba na kasar Syria. Ban Ki-moon ya nuna yabo ga kokarin da gwamnatin kasar Syria ta yi kan wannan lamari, kana ya nuna yabo ga kasashe membobin MDD na nuna goyon baya ga aikin da tawagar wakilan kungiyar haramta makamai masu guba da MDD suka yi. Ban da wannan kuma, Ban Ki-moon ya kalubalanci kasar Syria da ta tabbatar da cewa an lalata dukkan makamanta masu guba.

Kasashe da dama ne suka shiga aikin lalata makamai masu guba na kasar Syria, a ciki, kasashen Denmark da Norway suka dauki nauyin jigilar makaman ta jiragen ruwa, sa'an nan kasar Amurka ta lalata su a kan teku, Sin da Rasha kuwa sun tura jiragen ruwan soja don ba da kariya.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China