in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata bangarorin da rikicin Syria ya shafa su dakatar da musayar wuta a tsakaninsu
2014-06-04 20:44:21 cri
A ranar 3 ga wata ne aka gudanar da babban zaben shugaban kasar Syria inda 'yan takara guda uku da suka hada da shugaba mai ci Bashar al-Assad suka fafata a babban zaben.

Dangane da haka, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ya bayyana a yau Laraba 4 ga wata cewa, ya zuwa yanzu, an kwashe sama da shekaru 3 ana ricikin kasar Syria, lamarin da ya sanya jama'ar kasar cikin yanayin tashin hankali. Don haka, abu mafi muhimmanci dake gaban gwamantin kasar Syria a halin yanzu, shi ne, a dakatar da hare-haren da kasar ke fama da shi cikin sauri, ci gaba da taron shawarwarin Geneva, fara gudanar da shirin mika mulki a kasar, don warware ricikin kasar ta hanyoyin siyasa cikin sauri. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China