in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya gabatar da manufofi shida da za su kai ga warware rikicin Syria
2014-06-21 16:37:55 cri
Jiya Jumma'a 20 ga wata, babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya gabatar da manufofi shida da za su kai ga warware rikicin kasar Syria, inda kuma ya yi kira ga gamayyar kasa da kasa da su dauki matakan da suka dace kan wannan batun, da kuma sa kaimi ga kwamitin sulhu na MDD da ya gudanar da shirin hana jigilar makamai zuwa kasar Syria.

Mr. Ban ya ce, ya zuwa yanzu, ricikin kasar Syria ya riga ya haddasa mutuwar mutane sama da dubu 150, kuma sama da rabin mutanen kasar sun rasa gidajensu, yawan 'yan gudun hijira da aka yi rajista ya kai kimanin miliyan 2.8.

Game da haka ne, Mr. Ban ya gabatar da manufofi shida ga gamayyar kasa da kasa da za su kai ga warware rikicin kasar Syria, da farko, ya ce, ya kamata a kawo karshen ricikin kasar, musamman ma hana shigar da makamai cikin kasar Syria, idan kwamitin sulhu na MDD ba zai iya cimma matsaya guda kan batun ba, ya kamata kasa da kasa su dauki matakai da kansu wajen hana jigilar makamai zuwa kasar Syria.

Sauran manufofin sun hada da, gamayyar kasa da kasa su dukufa wajen kiyaye jama'ar kasar Syria, daukar matakai wajen ciyar da yunkurin warware ricikin kasar gaba, kammala aikin lalata makamai masu guba cikin sauri da dai sauransu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China