in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masu tsattsauran ra'ayi sun hallaka mutane da dama a Iraqi
2014-08-17 16:25:15 cri
Rahotanni daga kasar Iraqi na cewa mayakan kungiyar ISIS masu rajin kafa daular Islama, sun hallaka Yazidawa marasa rinjaye su kimanin 80, baya ga wani malamin Sunni da wani jagoran al'umma da mayakan suka hallaka a sassan Arewaci da Gabashin kasar.

A cewar wani mai magana da yawun jami'an kasar tsagin kurdawa, mayakan kungiyar ta ISIS mai alaka da Al-Qaida, sun hallaka Yazidawan ne a gidan wani jagoransu dake kauyen Kocho, mai nisan kilomita 100 yamma da birnin Mosul.

Jami'in tsaron ya kuma shaidawa manema labaru cewa mayakan na ISIS sun hallaka mutanen ne saboda sun ki su rungumi addinin musulunci.

Kaza lika wannan jami'i ya ce akwai wasu mutanen su sama da 200, da suka hada da mata da kananan yara, da 'yan ISISn din suka yi garkuwa da su daga kauyen Tal Afar dake karkashin ikon su.

Kafin hakan dai rahotanni sun tabbatar da cewa mayakan wannan kungiya ta masu kaifin kishin Islama, sun samu nasarar kwace garin Sinjar mai rinjayen Yazidawa, matakin da ya tilasawa al'ummun garin da ma na kauyukan dake kewayen sa arcewa zuwa tsaunukan dake kewayen yankin, da wasu garuruwa masu kusanci da yankin Kurdistan. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China