in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iran da Saudiyya sun nuna goyon baya ga sabon firaministan kasar Iraki
2014-08-13 15:51:25 cri
Shugaban kasar Iraki Muhammad Fuad Masum ya nada dan takarar kawancen jam'iyyun Shi'a kuma mataimakin shugaban majalisar dokokin kasar Haider al-Abad a matsayin sabon firaministan kasar. Game da hakan kasashen Iran da Saudiyya suka yi maraba da wannan nadin sabon faraministan a ranar 12 ga wata.

A wannan rana, sakataren hukumar tsaron kasar Iran Ali Shamkhani ya taya al-Abad murnar nada shi a matsayin sabon firaministan kasar Iraki, kana ya yi kira ga jam'iyyun siyasa daban daban na kasar Iraki da su hada kai don tinkarar barazana daga kasashen waje. Wannan ne karo na farko da kasar Iran ta bayyana ra'ayinta kan nada sabon firaminista a kasar Iraki.

Sarkin kasar Saudiyya Abdullah Bin Abdul-Aziz ya aiko da sakon taya murna ga sabon firaministan kasar Iraki, inda ya ce, yana fatan kasar Iraki za ta mai da hankali wajen hadin kai a tsakanin kungiyoyin addini da kabilu daban daban a matsayin tushen tabbatar da zaman lafiya a kasar a karkashin jagorancin al-Abad. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China