Shugaba ya bayyana hakan ne a jawabin da ya gabatar a daren Alhamis, inda ya bayar da umarnin daukar matakan kai hari ta sama idan har akwai bukatar yin haka kan mayakan kishin Islama da suka nausa zuwa yankin Kurdawa na kasar ta Iraki inda suka kame madatsar ruwa mai girma ta kasar.
Bugu da kari shugaban ya sanar da cewa, Amurka ta jefo kayan abinci da ruwa ta sama kan wani tsaunin da ke arewacin kasar Iraki a ranar Alhamsi, inda mayakan suka killace wasu kananan kabilu. (Ibrahim)