in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Kamaru ta sha alwashin kokarin lalubo ma'aikata Sinawa da suka bace
2014-05-18 16:27:29 cri
Kakakin gwamnatin kasar Kamaru Issa Tchiroma Bakary,ya bayyanawa manema labaru cewa, kasar sa ta yi Allah wadai da harin da aka kai wa kamfanin kasar Sin dake aiki a arewacin kasar, za kuma ta dauki dukkanin matakan da suka wajaba domin gano inda ma'aikata Sinawa da suka bace suka shiga.

A cewar Bakary, har yanzu ba a samu wata kungiya da ta dau alhakin harin na ranar Jumma'a ba, sai dai kungiyar Boko Haram dake da sansani a Najeriya, ta kan kai hare-hare makamantan wadannan a arewacin kasar ta Kamaru musamaman a baya bayan nan. Ya ce hukumokin Kamaru za su yi bincike kan bayanan da suka samu kafin su fidda sanarwa kan batun.

Wasu dakarun da ba a san ko su waye ba ne dai suka kai hari harabar wani kamfanin kasar Sin dake arewacin kasar ta Kamaru, lamarin da ya sabbaba jikkatar wani ma'aikaci Basine 1, tare da bacewar wasu ma'aikatan su 10.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China