in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya nuna bacin rai game da hare haren EIIL kan kananan kabilu a Iraki
2014-08-08 10:37:56 cri
Babban sakataren janar na MDD, Ban Ki-moon, ya bayyana matukar damuwarsa a ranar Alhamis game da hare-haren mayakan daular musulunci na EIIL suke kai wa kananan kabilu a kasar Iraki. A cewar MDD, an kai hare hare a ranar Alhamis a biranen Kirkouk da Qaraqosk, wadanda suka biyo bayan wasu hare-haren da aka kai a yankunan Tal Afar da Sinjar.

Rahotonni sun nuna cewa 'yan kabilar Yezides na ci gaba da kwarara zuwa kan iyakar Turkiya, yayin da wasu rahotannin kuma suka bayyana cewa akwai miliyoyin jama'a dake cikin tsaka mai wuya a yankunan tsaunukan Sinjar dake bukatar taimakon jin kai cikin gaggawa, matsala ce dake ta da hankali kuma ta gaggawa, in ji kakakin Ban Ki-moon a cikin wata sanarwa.

Shugaban MDD ya kira ga gamayyar kasa da kasa musamman ma masu fada a ji da kuma halin da ake ciki ba su damar kawo wani ci gaba mai kyau kan wannan matsala, su tallafawa gwamnati da al'ummar Iraki da kuma yin duk wani kokari wajen ganin an taimaka ga kawo karshen wahalar mutanen da wannan rikici na yanzu ya shafa a Iraki. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China