in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mozambique ta doke Tanzania 2-1 a wasan share fagen gasar AFCON
2014-08-07 19:55:00 cri
A ci gaba da buga wasannin fidda kasashen da za su buga kasar cin kofin kwallon kafar nahiyar Afirka na shekarar 2015, kulaf din kasar Mozambique ya doke takwaransa na Tanzania da ci 2-1, ya yin wasan da suka buga a ranar Lahadi.

Wannan dai nasara da Mozambique ta samu kan Tanzania a birnin Maputo, ya ba ta damar dara Tanzania da tazarar maki 4 da 3, za ta kuma buga zagayen wadannan wasanni na biyu.

Dan wasan Mozambique din Josemar ne dai ya ci wa kulaf din na sa kwallon farko, ana daf da tafiya hutun rabin lokaci, kafin a farke ta, kana Mozanbique din ta samu damar kara kwallo ta 2.

A cewar kocin kungiyar ta Mozambique Joao Chissano, sun sadaukar da wannan nasara da suka samu ga al'ummar kasar wadanda ke baiwa kungiyar cikakken goyon baya a ko da yaushe.

Shi kuwa a nasa bangare kocin Tanzania Mart Nooij, wanda a baya ya taba horas da kungiyar Mozambique, cewa ya yi dan wasan Mozambique Elias Pelembe Domingues, ya baiwa kungiyar sa gagarumin taimako a nasarar da kulaf din sa ya samu a wancan wasa.

A takaice dai Nooij ya ce 'yan wasan Mozambique sun taka rawar gani wajen dorewar nasarar da suka samu a wannan wasa.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China