in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi allah wadai da harin da aka kai a Lebanon
2014-02-02 16:16:06 cri
A Jiya Asabar 1 ga watan Fabrairu ne, kwamitin sulhu na MDD da kuma babban magatakardan majalisar Ban Ki-Moon suka ba da sanarwa, inda suka yi allah wadai da hare-haren boma-bomai da aka kai a gabashin kasar Lebanon, tare da nuna matukar damuwa kan karuwar rikice-rikice a kasar kwanan baya.

A Jiya Asabar ne wasu bama-bamai da aka dana cikin wasu motocin suka fashe a garin Hull Muller na gabashin kasar Lebanon dake kusa da yankin iyakar kasar Syria, wanda ya haddasa a kalla mutuwar mutane guda 4, yayin da mutane sama da 20 suka jikkata.

Sanarwar da kwamitin sulhu na MDD ya bayar, ta yi kira ga dukkan 'yan kasar da su hada kai wajen yaki da dukkan ayyukan da za su lalata zaman karko na kasar, ta kuma jaddada muhimmancin kiyaye manufar rashin tsoma baki a rikicin Syria.

Bugu da kari, Mr. Ban Ki-moon ya kuma ba da sanarwa ta hannun kakakinsa, inda ya yi kira ga jama'ar kasar Lebanon da su nuna goyon baya ga hukumomin gwamnatin kasar da suka hada da rundunar sojan kasa da kuma sojojin tsaron kasa, wannan ita ce hanyar da ta fi dacewa wajen kiyaye tsaro da zaman karko na wannan kasa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China