in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya mika sakon alhini ga shugabannin Aljeriya da Faransa
2014-07-28 20:43:58 cri
Kwanan baya, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aike da sakon alhini ga shugaban kasar Aljeriya da na kasar Faransa ta wayar tarho dangane da jirgin saman kasar Aljeriya da ya yi hadari a makon da ya gabata.

Cikin sakon da ya aika wa shugaban kasar Aljeriya, Mr. Xi ya nuna bacin rai game da rasuwa da jikkatar mutane sakamakon hadarin, a madadin gwamnati da jama'ar kasar Sin, shugaba Xi ya mika ta'aziya ga wadanda suka rasu, tare da jajantawa iyalen wadanda suka rasa rayukansu cikin wannan hadari.

Kana cikin sakon da ya aika wa shugaban kasar Faransa, Mr. Xi ya bayyana cewa, labarin rasuwar 'yan kasar Faransa da dama sakamakon hadarin jirgin saman na kasar Aljeriya mai lamba AH517 ya tayar masa da hankali sosai, kuma a madadin gwamnati da jama'ar kasar Sin, yana nuna matukar juyayi ga iyalen wadanda suka rasa rayukansu cikin wannan hadari.

Saboda kyakkyawan zumunci da ke tsakanin al'ummar kasar Sin da jama'ar kasar Faransa, wannan ya sa yanzu haka jama'ar kasar Sin ke kasance wa tare da jama'ar kasar Faransa wajen tausaya musu kan lamarin da ya faru. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China