in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a yi bincike kan hakikanin dalilin a hadarin jirgin saman Algeria bisa iyakacin kokari, in ji shugaban Mali
2014-07-26 16:49:46 cri
A jiya Jumma'a 25 ga wata, shugaban kasar Mali, Ibrahim Boubacar Keita ya bayyana cewa, za a yi iyakacin kokari domin yin bincike kan hakikanin hakikanan dalilan da suka haddasa hadarin jirgin saman fasinja na Algeria lambar AH5017. Mista Keita ya ce, a matsayinsa na shugaban kasar, abin da zai iyar yi shi ne kai ziyara a wurin hadarin, da mika ta'aziya ga iyalan fasinjojin da suka mutu, tare da nuna goyon baya ga kasashen da abin ya shafa tare da jaddada cewa, Mali za ta dauki duk wasu matakai domin tabbatar da aikin gano gawawwaki da jigilarsu zuwa kasashensu.

Kamfanin dillancin labaru na gwamnatin Algeria ya ba da labarin cewa, jirgin saman fasinja na Algeria ya fada a garin Gossi dake arewa maso gabashin kasar Mali. An gano tarkacen jiragen saman a sassafen ranar 25 ga wata. Bayan haka, a wannan rana ministan harkokin waje na Faransa, Laurent Fabius ya tabbatar da cewa, babu wanda ya tsira a cikin wannan jirgin saman. Fabius ya ce, bayan hadarin jirgin saman a Mali, masu aikin ceto na Faransa sun riga sun isa wurin hadarin domin fara aikin ceto da bincike. A tsakiyar ranar 25 ga wata, gidan talibijin Faransa ya gabatar da wani bidiyon, dake nuna tarkacen jiragen saman a cikin hamadar sahara.

Dadin dadawa, shugaban Algeria, Abdelaziz Bouteflika ya sanar da shiga zaman makoki har kwanaki uku a duk fadin kasar, domin nuna juyayi ga wadanda suka mutu a hadarin. Haka ma Burkina -Faso an yi zaman makoki na tsawon kwanaki biyu daga ranar 25 ga wata, domin nuna ta'aziya ga 'yan kasar da suka mutu a hadarin jirgin saman Algeria a ranar 24 ga wata.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China