in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojan kiyaye zaman lafiya a Mali ta Sin ta taimakawa kyautata batun hadarin jirin saman fasinja na Algeria
2014-07-26 16:30:06 cri
A jiya Jumma'a 25 ga wata da misalin karfe 11, bisa agogon wurin, bisa umurnin tawagar daidaita batun Mali ta MDD, rukunin sojojin injiniyoyi na rundunar sojan kiyaye zaman lafiya ta Sin a Mali ya tashi zuwa yankin Gao na Mali cikin gaggawa, domin taimakawa kyautata batun hadarin jirgin saman fasinja na Aljeriya mai lamba AH5017, tare da ba da agajin jin kai. An labarta cewa, wannan ne karo na farko da rundunar sojan kiyaye zaman lafiya ta Sin ta shiga aikin kyautata batun hadarin jirgin sama da ba da agajin jin kai bayan da aka tura ta zuwa ketare.

Shugaban rukunin sojojin injiniyoyin Sin da aka tura zuwa Mali a karon farko, Li Kaihua ya gaya wa wakilinmu cewa, wurin da jirgin saman Algeria ya fada, wato garin Gossi, yana da tazarar kilomita 60 daga birnin Gao, wurin da sansanin rundunar sojan kiyaye zaman lafiya ta Sin yake. Wurin ya kasance cikin yankin hamada ne, inda ake samun mazauna kadan. Kana hanyoyi sun lalace sosai a wannan yanki. A sabili da haka, akwai babban cikas wajen gudanar da aikin ceto da bincike kan hadarin.

Bisa umurnin kungiyar aikin ceton jirgin saman Algeria da ya yi hadari da tawagar daidaita rikicin Mali ta MDD, rukunin sojojin injiniyoyi na rundunar sojan kiyaye zaman lafiya ta Sin a Mali zai dauki nauyin dake bisa wuyansa na jigilar gawawwakin fasinjojin da suka mutu tare da rundunar sojan Faransa dake Mali.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China