in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kira taron ministoci karo na 17 na kungiyar 'yan ba ruwanmu a kasar Algeria
2014-05-27 14:30:07 cri
An kira taron ministoci karo na 17 na kungiyar 'yan ba ruwanmu a ranar Litinin 26 ga wata a Algiers, babban birnin kasar Algeria, bisa taken "inganta hadin gwiwa don neman samun zaman lafiya da wadata".

Ramtane Lamamra, ministan harkokin waje na kasar Algeria ya bayyana a yayin bikin kaddamar da taron, cewar a halin yanzu dai, duniya na cikin wani hali na rudani, kasashe da dama na tinkarar hare-haren ta'addanci, da na manyan laifuffukan kasa da kasa a sassa daban daban na duniya. Dalilin haka ne, ya kamata kasashe membobin kungiyar 'yan ba ruwanmu su dauki matakai don inganta hadin gwiwarsu, a kokarin ciyar da irin wannan sabon sauyin da aka samu a cikin dangantaka a tsakanin kasa da kasa.

Mr. Lamamra ya jaddada cewa, kungiyar 'yan ba ruwanmu ta samar da wata kyakkyawar dama ga kasashe masu tasowa wajen cudanya a tsakaninsu, a matsayin wata dama inda kasashe masu tasowa suke iyar cimma matsaya daya kan dimbin lamura, da kuma yin shawarwari tare da kasashe masu ci gaba cikin adalci.

A tsawon taron, kasashe membobin kungiyar da ministoci da jami'ai da kuma kwararru na kasashe 'yan kallo za su mai da hankali kan batutuwan da ke jawo hankulansu a fannonin siyasa, tattalin arziki da kuma tsaro tare da fitar da wata sanarwar karshe. (Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China