in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bada rahoton yiwuwar bullar cutar Ebola a Najeriya
2014-07-25 20:38:24 cri
An samu wani dan asalin kasar Liberia mai shekaru 40 da haihuwa da ake tuhumarsa da dauke da cutar Ebola bayan isar sa jihar Ikko daya daga cikin jihohin da yafi yawan al'umma a tarayyara Najeriya,kamar yadda jami'an kiwon lafiya suka sanar a ranar alhamis.

An dai samu bayanan hakan ne daga wani asibiti mai zaman kanshi a jihar inji mai bada shawara na musamman ma gwamnana jihar kan harkokin kiwon lafiya,Yewande Adeshina lokacin da take bayani ga manema labarai.

A cewar Madam Adeshina, yanayin jikin mara lafiyan ya nuna cuta ta kama shi sosai,abin da yasa nan take wuraren kula da kiwon lafiya a jihar suka fitar da sabon tsari na koyar da yadda mutane zasu kula da lafiyar su domin guje ma kamuwa da cutar da kuma kariya ga sauran jama'a. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China