in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An dakatar da jami'an hukumar kwallon kafa 15 bisa zargin sayar da wasa a Saliyo
2014-07-23 18:09:22 cri
Ma'aikatar wasannin kasar Saliyo, da hukumar wasan kwallon kafa ta kasar, sun dakatar da wasu jami'an hukumar wasan kwallon kafar kasar su 15, sakamakon zargin da ake musu na sayar da wasan share fagen gasar cin kofin duniya na shekarar 2010, da ya gudana tsakanin Saliyo da Afirka ta Kudu a wancan lokaci.

An gudanar da wannan wasa ne dai a ranar 21 ga watan Yulin shekarar 2008, inda bangarorin 2 suka yi kunnen doki maras ci, abin da ya sanya Saliyo ta kasa samun damar ci gaba zuwa gasar cin kofin duniya da aka gudanar a Afirka ta Kudu.

Dangane da wannan batu, ma'aikatar wasanni, da hukumar gudanar da wasannin kwallon kafa ta kasar Saliyo, sun ce sun tabbatar da samun cikakkun shaidu, kan yadda wasu jami'ai suka aikata mabudi, na sayar da wancan wasa, lamarin da a cewar hukumomin ya sabawa dokoki, da akidar wasanni da ma kishin kasa.

Saboda haka, hukumomin suka yanke shawarar dakatar da jami'an daga aikin su, da suka hada da 'yan wasa 5 dake buga ma kungiyar kwallon kafar kasar wasa, da darakta mai kula da wasanni Alphan Koker, da alkalai 3, da wani mai kulob din wasan kwallon kafa, da wani koci mai horar da 'yan wasa, da mambobin hukumar wasan kwallon kafar kasar su 3, gami da wani dan Lebanon mai kula da kungiyar wasan kwallon kafa.

Yanzu haka dai an riga an kafa wani kwamitin musamman domin gudanar da bincike kan wannan batu, sai dai ba a bayyana wa'adin aikin kwamitin ba tukuna.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China