in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
FIFA na shirin fuskantar amsa kiran kotu
2014-05-20 15:03:50 cri
Yayin da ake ci gaba da dakon yadda za ta wakana, game da shirin da mahukuntan kasar Brazil ke yi, na tabbatar da gudanar gasar cin kofin duniya na bana lami lafiya, a hannu guda kuma kungiyar 'yan kwallon kafar kasar ta Brazil FENAPAF, ta ce zata gabatar da wasu bukatun ta gaban kotu, da suka hada da neman a matsawa FIFA sauya lokutan gudanar wasu wasanni, tare da sanya dan lokacin hutu cikin kowane rabin lokacin wasa, domin baiwa 'yan wasa damar sararawa, duba da binciken dake nuna hadarin dimamar yanayin zafin jiki, da 'yan wasa za su iya gamuwa da shi yayin gasar dake tafe.

Cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Asabar, FENAPAF ta ce za ta mika wannan koke na ta gaban kotu a ranar Litinin mai zuwa. Kaza lika sanarwar mai dauke da sa hannun jagoran FENAPAF Rinaldo Martorelli, ta ce za ta bukaci a sauya lokutan wasannin da za a fara su tsakanin karfe 1 zuwa karfe 3 na yamma bisa agogon kasar, a yankunan Arewaci, da Arewa maso Gabashi, da kuma tsakiyar yammacin kasar, lokutan da a cewar kungiyar, ba za su dace da kariyar da ya kamata a baiwa lafiyar 'yan wasan ba.

Game da batun sanya lokacin sararawa ga 'yan wasa a cikin lokacin wasannin kuwa, sanarwar ta ce hakan na da nasaba da gwajin da aka yi a biranen Brasilia, da Manaus, da Frotaleza, da Sao Paulo, a watannin Yuni da Yulin bara, gwajin da ya nuna cewa awon zafin jikin 'yan wasa na iya haura digiri salsos 40, wanda hakan ke da hadari ga lafiyar su.

Kawo yanzu dai FIFA ba ta ce komai game da wannan batu ba tukuna.

Za dai a buga daukacin wasannin gasar cin kofin na duniya ne daga ranar 12 ga watan Yuni, ya zuwa 13 ga watan Yulin dake tafe.

Bisa kuma awon matsakancin yanayin zafin biranen kasar, birnin Manaus ne ke kan gaba a fannin zafi da digiri salsos 31, sai Cuiaba mai digiri salsos 30.7, sai Fortaleza mai digiri salsos 29.3, da Natal mai digiri salsos 29, yayin da kuma birnin Recife ke da digiri salsos 28.8. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China