Lubowa ya ce a yanzu haka sun yi shirin kai 'yan wasan na su birnin Jinja, domin su saba da yanayi, wanda ya yi kusa da na kasar Seychelles gabanin wasan na su da kasar Seychelles din a ranar 14 ga watan Yunin nan.
Har ila yau jami'in hukumar ya bayyana sunan Matia Lule a matsayin babban kocin kungiyar matasan.
Bisa tsarin wannan gasa dai kungiyar da ta samu nasara tsakanin Uganda da Sychelles ce za ta kara da kasar Rwanda a zagayen gasar na gaba.