in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bukaci amfani da karfi wajen kawo karshen boren 'yan tawaye a Mali
2014-05-20 20:14:45 cri
Galibin 'yan siyasar kasar Mali sun yi allah wadai da fadan da ya barke ranar Asabar tsakanin sojoji da 'yan tawayen da ke neman 'yancin yankin Azawad (MNLA), inda suka nemi hana ziyarar da firaministan kasar Moussa Mara ya shirya kaiwa zuwa yankin Kidal da ke arewacin kasar.

Bayanai na cewa, harin da 'yan tawayen suka kai kan sojojin ya haddasa mutuwar mutane 36, lamarin da ya saba wa yarjejeniyar Ouagadougou da aka sanya hannu a kai a watan Yunin shekarar 2013 tsakanin gwamnatin rikon kwaryar kasar da kungiyoyin 'yan tawayen.

Sai dai bayan dawowarsa birnin Bamako, firaministan ya bayyana cewa, yanzu kasar ta shiga yaki da 'yan tawayen na MNLA, inda ya bayar da umarnin tura karin dakaru zuwa yankin.

Ya ce, an dauki wannan mataki ne domin kawo karshen matsayin kawo sarki da garin ke fuskanta tun lokacin da 'yan tawayen suka fara tayar da kayar baya a watan Janairun shekarar 2012. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China