Ma'aikatar harkokin wajen kasar Rasha ta bayyana cikin wata sanarwa cewa, Rasha ba za ta yarda da duk wani kokari na shafa mata kashin kaji ba kuma tana da ikon daukar matakan da suka dace na mayar da martani.
Sanarwar ta ce, takunkuman da baitun malin Amurka ya sanya wa wasu 'yan kasar da manyan hukumomin kudi, makamashi da makaman kasar, da nufin daukar fansa game da abubuwan da ke faruwa a Ukraine batu ne da bai shafi Washington ba.
Shugaba Vladimir Putin na Rasha wanda yanzu haka ke Brazil ya bayyana cewa, takunkumin da aka sanya wa kasarsa, tamkar kaikayi ne zai koma kan mashekiya kuma zai raunata dangantakar da ke tsakanin Amurka da Rasha. Amma ya ce, har yanzu kofar tattaunawar Rasha a bude ta ke. (Ibrahim)