in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sin ya bayyana ra'ayinsa wajen gudanar da harkokin jihar Xinjiang
2014-05-30 10:59:42 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, ya kamata a gudanar da harkokin jihar Xinjiang bisa dokokin kasar yadda ya kamata, tabbatar da zaman karkon jihar cikin hadin gwiwa da kuma inganta aikin gina jihar cikin dogon lokaci. Game da haka ne, shugaba Xi ya jaddada cewa, ya kamata a gudanar da ayyukan gina jihar bisa tushen raya tattalin arziki da kyautata zaman rayuwar al'ummomin jihar, musamman ma kan ciyar da hadin kan al'ummomin gaba da kuma hana yaduwar tsattsauran ra'ayin addini, ta yadda za a iya gina jihar Xinjiang bisa tsarin gurguzu na hadin kai, zaman jituwa da kuma samun wadata.

Shugaba Xi Jinping ya bayyana hake ne a yayin taro na biyu na tattaunawa kan ayyukan gina jihar Xinjiang da aka yi a nan birnin Beijing daga ranar 28 zuwa ta 29 ga watan. Bugu da kari, shugaba Xi ya kara da cewa, manyan ayyukan kasar Sin wajen gina jihar Xinjiang su ne, tabbatar da zaman karko a jihar da kuma samun dauwammamen ci gaban jihar. Dole a mai da aikin yaki da aikace-aikacen ta'addanci da na tashin hankali a matsayin aiki mafi muhimmaci a halin yanzu, a sa'i daya kuma, a karfafa hadin gwiwa tare da kasashen duniya wajen yaki da ta'addanci. Game da haka, ya kamata a kara kokari bisa dogaro da karfin kabilu daban daban na kasar, da zurafafa mu'amalar dake tsakaninku, ta yadda za a samu unguwanni masu zaman lafiya dake kunshe da kabilu daban daban. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China