in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wata babbar jami'ar harkokin hakkin bil'adam ta MDD ta yi kira da'a kiyaye fararen hula yayin rikicin Palestinu da Isra'ila
2014-07-12 16:41:19 cri
Ofishin hakkin bil'adam na MDD a Geneva ya yi kira a ranar Jumma'a ga Palestinu da Isra'ila da su bi ka'idojin hakkin bil'adam da na jin kai na duniya, domin kiyaye mamagance kai wa fararen hula hare hare.

A cikin sanarwar da aka gabatar a wannan rana, babbar jami'ar harkokin hakkin bil'adam ta MDD, madam Navanethem Pillay ta nuna damuwarta sosai kan cewa, Palestinu da Isra'ila na nuna wa junansu karfin tuwo, kuma hakan ya janyo mutuwar mutane da kawo illa ga zaman lafiya da rashin amincewa da juna, abin da ya kara tsananta rikicin.

Madam Pillay ta jaddada cewa, kowane irin matakan soja, bai kamata ya kawo illa ga fararen hula ba, kuma bai kamata a kai hari ga muhallinsu ba. Jami'ar ta yi allawadai da hare-haren da suka haddasa mutuwa da jikkatar fararen hula, ciki har da kananan yara da mata, tare da yin kira ga bangarorin biyu da su tsagaita bude wuta nan take, domin daidaita wannan matsala cikin lumana.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China