in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya na taimakawa Liberiya wajen yaki da annobar Ebola
2014-07-12 16:06:47 cri
Tarayyar Najeriya ta sanar da taimakon kudi na dalar Amurka dubu dari biyar domin taimakawa Liberiya wajen yakin da take da annobar Ebola, a cewar wata sanarwa a ranar Jumma'a.

Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan ya yi wannan sanarwa a yayin taron kungiyar ECOWAS karo na 45 a birnin Accra na kasar Ghana.

Hakan ya biyo bayan kaddamar da gidauniya ta musammun a yayin wannan taro domin yaki da yaduwar kwayoyin cutar Ebola a shiyyar, wannan taimako ya cimma dalar Amurka miliyan 3,5 da Nijeriya ta baiwa Guinee, Sierra Leone, kungiyar kiwon lafiya ta yammacin Afrika (OOAS) da kuma asusun hadin gwiwa na ECOWAS kan yaki da cutar Ebola.

A Liberiya an samu mutane 87 da suka mutu daga cikin mutane 131 da suka kamu da cutar da aka tabbatar in ji mataimakin shugabar kasar Liberiya, Joseph Boakai a yayin taron.

A Liberiya, Guinee da Sierra Leone, kasashen da cutar Ebola ta fi tsanani ya zuwa yanzu an kiyasta mutane 844 suka kamu da cutar yayin da mutane 518 suka mutu a cewar darektan kungiyar OOAS, Xavier Crespin.

Ana bukatar kimanin dalar Amurka miliyan 15 domin yaki da cutar Ebola ganin yadda take kamari a cikin wadannan kasashe uku da kuma hana yaduwarta zuwa sauran kasashen yammacin Afrika in ji mista Crespin. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China