in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Bouteflika ya bukaci a bar Halilhodzic ya ci gaba da kasancewa kocin kungiyar Aljeriya
2014-07-11 16:23:12 cri
Shugaban kasar Aljeriya, Abdelaziz Bouteflika, ya yi kira ga shugaban hukumar gudanarwar kwallon kafar kasar sa FAF Mohamed Raouraoua, da ya bar kocin kungiyar kasar Vahid Halilhodzic, ya ci gaba da kasancewa mai horas da 'yan wasa, sakamakon kwazon da ya ce 'yan wasan kasar su ka nuna, a wasannin da suka buga yayin gasar cin kofin kwallon kafa na duniya da yanzu haka ake yi a Brazli.

Shugaba Bouteflika wanda ya bayyana hakan ya yin da ya taryi shugaban hukumar ta FAF, da kocin kasar Halilhodzic a ofishin sa, ya taya su murna, sakamakon abin da ya kira kata rawar gani da kulaf din kasar ya yi, kafin wasan su na karshe da kasar Jamus, wanda Jamus din ta lashe da ci 2 da 1.

A baya dai ana rade-radin mai yiwuwa ne koci Halilhodzic, ya sauya sheka zuwa wani kulaf din na daban, duba da yadda tun a watan Afirilun da ya gabata hukumar ta FAF ta bukaci ya sake sabunta kwantiragin sa, amma ya ce sai bayan gasar cin kofin na duniya.

Bugu da kari akwai batun kalamai dake nuna yiwuwar ya koma kulaf din Trabzonspor FC na Turkiyya.

Hakan dai na zuwa ne a gabar da shi kan sa shugaban hukumar ta FAF Raouraoua ke shaidawa 'makarraban sa, aniyar kammala batun wanda zai kasance mai horas da 'yan wasan kungiyar kasar, gabanin fara buga wasannin share fagen gasar cin kofin nahiyar Afirka, da za a yi a kasar Morocco tun daga watan Satumbar shekarar 2015 mai zuwa.

A hannu guda kuma akwai batun da ake yi cewa tuni Raouraoua ya nemowa kasar sabon koci, dan kasar Faransa mai suna Christian Gourcuff, wanda kuma shi ne mai horas da 'yan wasan Lorient FC a halin yanzu. Koda yake dai mai yiwuwa wannan batu ya gamu da cikas, sakamakon bukatar da shugaban kasar ta Aljeriya ya bayyana.

A ranar Labara ne dai tawagar 'yan wasan Aljeriyar ta isa gida, in da aka yi mata tarba ta musamman, kafin daga bisani shugaban Bouteflika ya gana da su, in da kuma ya bayyana mu su matukar gamsuwar sa da yadda suka taka leda a gasar ta bana. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China