in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban FIFA ya bukaci a karawa kasashen Afirka da Asiya gurabe a gasar cin kofin duniya
2014-07-09 09:56:00 cri

Shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya (FIFA) Sepp Blatter ya ce, guraben da ake kebe wa kasashen Afirka da Asiya a gasar cin kofin kwallon kafa na duniya sun kasa, idan aka yi la'akari da yawan kungiyoyin kwallon kafa da nahiyoyin ke da su a hukumomin kwallon kafan biyu.

Blatter ya bayyana hakan ne cikin sharhin da ya rubuta a mujallar da hukumar ta FIFA ke wallafa wa mako-mako, inda ya ce, akwai bukatar a duba yawan guraben da ake baiwa ko wace nahiya.

Shugaban na FIFA ya kuma yaba rawar da kasashen Afirka, arewaci da tsakiyar Amurka suka taka a gasar ta bana, inda a karon farko kasashe biyu daga nahiyar ta Afirka suka kai ga zagaye na biyu na gasar.

Bisa tsarin FIFA na yanzu, kasashen Afirka na da gurabe 5 ne yayin da nahiyar Turai ke da gurabe 13. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China