Gwarzon 'dan kwallon kafan duniya kuma 'dan wasan kasar Argentina Lionel Messi ya ce, kasar tana dab da lashe kofin kwallon kafa na duniya na bana da ake fafata wa a kansa a kasar Brazil.
Messi ya yi wannan hasashe ne a shafinsa na sada zumunta na Facebook, inda ya ce, sun sadaukar da nasarar da suka samu a wasan ranar Laraba da suka doke Netherlands da ci 4 da 2 a bugun daga kai sai mai tsaron gida ga marubucin labaran wasannin nan 'dan kasar Argentina Topo Lopez da ya mutu sanadiyar hadarin mota a Sao Paulo a ranar da aka buga wannan wasa.
Yanzu dai Argentina za ta kara da Jamus ranar Lahadi a wasan karshe da za a yi a filin wasan na Maracana. (Ibrahim)