in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin gwamnatin kasar Ukraine sun kwace kashi 2 cikin kashi 3 na jihohi biyu dake gabashin kasar
2014-07-11 10:11:31 cri
Wani jami'in kasar Ukraine ya bayyana a jiya Alhamis 10 ga wata cewa, sojojin gwamnatin kasar sun riga sun kwace kashi 2 cikin kashi 3 na jihohin Donetsk da Luhansk dake gabashin kasar.

Sakataren hukumar tsaron kasar Ukraine Andrey Parubii ya bayyana a wannan rana cewa, sojojin gwamnatin kasar sun kwace ikon yankuna 23 cikin yankuna 36 na jihohin biyu, yanzu yawan yankunan da ke hannun 'yan aware ya ragu sosai a cikin mako guda da ya wuce.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Rasha Alexander Lukashevich ya bayyana wa taron manema labaru a wannan rana cewa, aikin dake gaban kome wajen warware rikicin Ukraine shi ne aiwatar da yarjejeniyar da ministocin harkokin wajen kasashen Rasha, Jamus, Faransa da Ukraine suka cimma a ranar 2 ga wata, da kuma tsagaita bude wuta cikin hanzari.

A nata bangare ma'aikatar harkokin wajen kasar Rasha ta bayar da wata sanarwa a wannan rana, inda ta yi allah wadai da harin da sojojin kasar Ukraine suka sake kai kan tashar binciken ababan hawa dake kan iyakar Rasha da Ukraine. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China