in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya ya yi kira ga sabbin hafsoshin soja da karfafa yaki da ta'adanci
2013-09-15 16:20:13 cri
Shugaban tarayyar Najeriya Goodluck Jonathan yayi kira a ranar Asabar ga sabbin hafsoshin sojojin kasar da su karfafa kwarin gwiwa wajen yaki da ta'adanci da kuma rashin tsaro a cikin kasar bayan ya halarci wani bikin karshen karatu na hafsoshin na makarantar tsaro ta Najeriya dake jihar Kaduna a arewacin kasar.

Najeriya na fama da ayyukan ta'adanci dake da hannun 'yan kishin islama na kungiyar Boko Haram wadanda suka janyo mutuwar mutane fiye da dubu daya da dari biyar, wadanda yawancinsu mata da yara tun daga bakin shekarar 2009.

Shugaba Jonathan ya jaddada a yayin wannan biki cewa sabbin hafsoshin ya kamata su gudanar da muhimmin aiki wajen kawo sauyi ga rundunar sojojin Najeriya bisa tsarin da ya shafi sauye sauyenta.

Haka kuma ya bayyana cewa hukumarsa ta dauki niyyar bunkasa harkokin tsaro da shari'a, tare da gayyatar wadannan sabbin hafsoshin da suka gama karatu da su yi amfani da ilmin da suka samu wajen kawo sauyin cikin aikinsu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China