in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Najeriya sun sanar da fatattakar magoya bayan kungiyar nan ta Boko Haram
2013-10-26 16:31:27 cri
Rundunar Sojoji a tarayyar Najeriya ta tabbatar da gudanar da wasu ayyukan soji a 'yan kwanakin nan, don fatattakar 'ya'yan kungiyar masu kaifin kishin Islaman da aka fi sani da Boko Haram a jihohin Borno da Yobe, dake arewa maso gabashin kasar. Rundunar wadda ta tabbatar da hakan a ranar Juma'a 25 ga watan nan, ta bayyana harbe wasu daga dakarun kungiyar kusan dari 1.

A yayin da yake ba da sanarwar, kakakin rundunar sojojin Najeriyar Mohammed Dole, ya ce, an yi amfani da jiragen saman yaki, don kai hari ga wata makarfafar 'ya'yan kungiyar ta Boko Haram, inda aka kashe dakarun kungiyar 74, yayin da wasu da dama suka tsere da raunuka.

A cewar Dole, sojojin gwamnati 2 ne suka ji rauni yayin wannan sumame, ba kuma a samu wani rahoto na rasa rayuka, ko jikkatar fararen hula ba.

Tun dai cikin watan Mayun wannan shekara ne shugaban kasar Najeriyar Goodluck Jonathan, ya sanar da kafa dokar ta-baci a jihohin Borno, da Yobe, da Adamawa, dake arewa maso gabashin kasar. Aka kuma jibge sojoji da dama a wadannan yankuna, don dakile ayyukan dakaru masu dauke da makamai dake goyon bayan kungiyar ta Boko Haram. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China