in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya isa birnin Seoul don fara ziyarar aiki a kasar Koriya ta Kudu
2014-07-03 14:53:57 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya isa birnin Seoul a yau Alhamis 3 ga wata, don fara ziyarar aiki a kasar Koriya ta Kudu.

A wannan rana kafin ya kama hanya Xi Jinping ya fitar da bayani ta kafofin jaridun The Chosun Ilbo, JOONGAN DAILY da kuma Donga Daily na kasar Koriya ta Kudu, inda ya bayyana cewa, a cikin shekaru 22 da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin kasashen biyu, a karkashin kokarin su, ana samun nasarori masu yawa kan hadin gwiwar kasashen a dukkan fannoni.

Shugaba na Sin ya ce kasashen biyu sun kasance kasashe masu samun moriya iri daya, sannan kuma sun zama abin misali na raya dangantakar abokantaka a tsakaninsu a fadin duniya.

Mr. Xi Jinping ya lura cewa, a halin yanzu akwai damar samun babban ci gaba kan dangantakarsu, don haka yadda za a kara inganta dangantakarsu shi ne muhimmin batun da za a tattauna lokacin ziyarar da zai yi a kasar Koriya ta Kudu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China