in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya tashi zuwa kasar Koriya ta Kudu
2014-07-03 10:49:12 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tashi daga nan birnin Beijing zuwa kasar Koriya ta Kudu da sanyin safiyar Alhamis din nan, domin fara ziyarar aiki ta kwanaki biyu a kasar Koriya ta Kudu.

Wannan ne dai karon farko da shugaba Xi zai gudanar da ziyara a kasar Koriya ta Kudu, tun bayan da ya dare karagar shugabancin kasar Sin, lamarin da kuma ya sanya ziyarar tasa janyo hankalin kasashen duniya.

Kaza lika ziyarar ta shugaba Xi a wannan karo, ta biyo bayan wadda takwararsa ta Koriya ta Kudun Park Geun-hye ta gudanar bara a nan kasar Sin. An ce Xi Jinping zai yi shawarwari tare da shugaba Park Geun-hye, sa'an nan zai gana da shugaban majalisar dokokin kasar Chung Ui-hwa, da kuma firaministan kasar Chung Hongwon.

Bugu da kari Xi, zai gabatar da jawabi a jami'ar Seoul, kana zai halarci tarukan tattalin arziki da cinikayya.

Kasashen duniya da dama dai na fatan samun kyakkyawan sakamako don gane da ziyarar shugaba Xi a wannan karo, tare da maida hankali a fannonin siyasa, da tattalin arziki, da cinikayya, da al'adu da dai sauransu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China