in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Ghana ya bukaci a gudanar da bincike game da rashin nasarar da Black Stars ta kwasa a bana
2014-07-02 15:32:07 cri
Shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama ya jaddada bukatar kafa wani kwamitin bincike, da zai nazarci dalilan da suka sanya kasar sa gaza tabuka wani abin a zo a gani, a gasar cin kofin duniya da ake bugawa a Brazil.

Wannan ne dai karon farko da Ghana ta kasa kaiwa ga zagaye na biyu na gasar cin kofin duniya a tarihin zuwan ta gasar, bayan da Portugal ta doke ta da ci 2 da 1 a wasan su na ranar Alhamis.

Da yake tsokaci game da hakan, shugaba Mahama ya ce akwai bukatar tantance musabbabin aukuwar wannan rashin nasara tun daga tushe, har ya zuwa lokacin buga wasannin da Ghanan ta kasa taka rawar gani a cikin su.

Daga nan sai shugaban na Ghana ya bukaci a yiwa kungiyar garan-bawul, yana mai baiwa al'ummar kasar hakuri kan abin da ya faru, tare da bukatar su da su ci gaba da baiwa kungiyar ta Black Stars goyon bayan da suka saba.

A bana dai kungiyar ta Ghana ta fuskanci tarin matsaloli, kama daga batun takaddamar kudade, da ta kusa kaiwa ga 'yan wasan kauracewa buga wasan su da Portugal, ya zuwa korar Sulley Ali Muntari, da Kevin-Prince Boateng, da mahukuntan kungiyar suka yi kafin wasan karshe.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China