in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kocin Najeriya Stephen Keshi ya yi murabus
2014-07-02 15:31:11 cri
Wasu rahotanni na cewa babban kocin kungiyar kwallon kafar Najeriya Stephen Keshi, ya yi murabus daga matsayinsa na mai horas da 'yan wasan kasar, bayan da aka fid da kungiyarsa daga gasar cin kofin duniya a ranar Litinin.

Kocin na Super Eagles mai shekaru 52 da haihuwa, wanda ya taba taka ma kungiyar kwallon kafan Najeriyar kwallo a matsayin dan wasan baya, ya sanar da kudurin da ya tsayar na komawa gida don fuskantar sabbin kalobaloli, bayan da kungiyar Faransa ta lashe kungiyarsa da ci 2 da nema.

Keshi dai ya fara horar da 'yan wasan kungiyar Najeriya ne a shekarar 2011, inda ya jagoranci kungiyar wajen lashe gasar cin kofin nahiyar Afirka. Kaza lika shi da Mahmoud El-Gohary dan kasar Masar ne kadai suka kasance mutane 2, kacal a nihiyar Afirka, da suka taba lashe kambin wannan gasa ta cin kofin Afirka a matsayin kociya, bayan sun daga kofin a matsayin 'yan wasan kungiyar su.

A lokacin ya na taka leda, Stephen Keshi ya ci ma kungiyar Najeriya kwallaye 64, tsakanin shekarar 1981 zuwa ta 1995, haka kuma ya taimakawa kungiyar samun nasarar daukar kofin nahiya Afirka a shekarar 1994 a kasar Tunisia.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China