in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Sin, Indiya da Myanmar sun yi bikin tunawa da cika shekaru 60 da sanar da manufar zama tare cikin lumana
2014-06-28 20:48:42 cri
Yau Asabar 28 ga wata, kasashen Sin, Indiya da Myanmar sun yi bikin tunawa da cika shekaru 60 da sanar da manufar zama tare cikin lumana a nan birnin Beijing, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi alkawari a gun bikin cewa, Sin na fatan samun ci gaba cikin annashuwa tare da sauran kasashen duniya, musamman ma kasashe makwabtanta.

Shugaban Sin Xi Jinping, da takwaransa na Myanmar U Thein Sein, da mataimakin shugaban kasar Indiya sun halarci wannan biki. A cikin jawabinsa, shugaba Xi ya bayyana ra'ayin Sin kan nacewa ga bin manufar zama tare cikin lumana da sa kaimi ga kafa sabuwar dangantaka tsakanin kasashen duniya a sabon zamani, ciki har da tsayawa tsayin daka kan tabbatar da adalci a fannin ikon mallakar kasa, tabbatar da tsaro tare da juna, samun bunkasuwa tare, yin hadin gwiwa domin samun moriyar juna da sauran manyan manufofi masu muhimmanci.

Bayan haka, shugaba Xi ya furta cewa, Sin za ta tsaya tsayin daka kan neman samun bunkasuwa cikin lumana, kuma babu wata kasar da za ta canza ra'ayinta ba ko kadan.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China