in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban jami'in kasar Amurka ya kai ziyara a Saudiya don tattauna yanayin da ake ciki a Iraki da Sham
2014-06-28 16:33:00 cri
Babban sakataren harkokin wajen kasar Amurka, mista John Kerry, ya isa birnin Jidda dake yammacin kasar Saudiya a ranar Jumma'a 27 ga wata, inda ya gana da sarkin kasar Abdullah Bin Abdul-Aziz, da Ahmad Jarba, shugaban wata kungiyar dake adawa da gwamnatin Sham, don tattauna yanayin da ake ciki a kasashen Iraki da Sham.

John Kerry ya nuna ma Ahmad Jarba cewa, yana fatan ganin kungiyarsa mai sasaucin ra'ayi za ta iya taka muhimmiyar rawa a kokarin dakile masu tsattsauran ra'ayi na 'kungiyar kasar Islama ta Iraki da Levant' a kasar Iraki. A nasa bangare, Ahmad Jarba ya ce, tabarbarewar yanayin da ake ciki a Sham da Iraki na bukatar kasashen Amurka da Saudiya su kara ba da goyon baya. Haka kuma, ya nuna rashin jin dadi ga firaministan kasar Iraki Nourial Maliki kan yadda ya kara tsananta rikicin da ake samu tsakanin 'yan darikar Shi'a da masu goyon bayan darikar Sunni a kasar.

Daga bisani, John Kerry ya je fadar sarkin dake Jidda, inda ya gana da sarki Abdullah Bin Abdul-Aziz, sai dai ba abin da aka fitar daga wannan tattaunawa tasu. Amma wasu kafofin watsa labaru sun sheda cewa dalilin ziyarar John Kerry a Saudiya shi ne domin neman kasar ta yi tasiri kan 'yan darikar Sunni dake kasar Iraki, don su shiga a dama da su a sabuwar gwamnatin da za a kafa a kasar Iraki, tare da neman Saudiya da ta kara taka muhimmiyar rawa don dakile kungiyar mai tsattsauran ra'ayi ta 'kasar Islama ta Iraki da Levant'. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China