in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta kudu da MDD sun lashi takwabin kawo karshen sanya yara soja
2014-06-25 20:39:33 cri
Majalisar dinkin duniya ta bayyana cewa,Sudan ta kudu ta nanata kudurinta na martaba shirin da ta sanya hannu a shekara 2012 da MDD don kawo karshen daukar yara tare da amfani da su a matsayin sojojin gwamnati ko wasu ayyukan da basu dace ba.

Wakilin musamman na babban sakataren MDD mai kula da harkokin yara da yake-yake Leila Zerrougui ne ya bayyana hakan yayin da ya kalli yadda aka cimma wannan yarjejeniya a ranar Talatar da ta gabata. Ya ce amfani da yara a tashe-tashen hankula yana da mummunan tasiri ga rayuwarsu,muddin ana bukatar gina makomar kasa, ya zama wajibi a kare su.

Manufar da ke kunshe cikin shirin, shi ne za a kare yara daga daukar su a matsayin sojoji da amfani da su da keta wasu abubuwa da suka sabawa doka a kowa ne lokaci, ciki har da lokutan da ake fama da tashe-tashen hankula ko rikici.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China