in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana shirin gudanar da zagaye na biyu na tattaunawar wanzar da zaman lafiya na Sudan ta kudu a Habasha
2014-02-10 20:24:12 cri
A yau ne ake sa ran fara tattaunawar wanzar da zaman lafiya zagaye na biyu tsakanin sassan da ke gaba da juna a Sudan ta kudu a birnin Addis Ababa na kasar Habasha.

Wata sanarwa da kungiyar raya gwamnatocin gabashin Afirka(IGAD) wadda ke shiga tsakanin tattaunawar ta bayar, ta bayyana cewa, za a fara tattaunawar ce da misalin karfe 5 na yamma agogon wurin.

Ana gudanar da tattaunawar ne,yayin da bangarorin biyu ke ikirarin mutunta yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma,duk da rahotannin da ake samu cewa, ana gwabza fada tsakanin bangarorin biyu a sassan daban-daban na jaririyar kasar.

Sanarwar kungiyar ta IGAD na cewa,tattaunawar za ta hallara gwamnatin Sudan ta kudu da kungiyar adawa ta SPLM wuri guda

A makon da ya gabata ne aka cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta da nufin daidaita rikicin siyasar da ake fama da shi a kasar, tsakanin shugaba Salva Kiir da tsohon mataimakinsa Riek Machar da aka tsige daga mukaminsa a watan Yulin shekarar 2013,kana aka zarge shi da yunkurin yin juyin mulki.

A ranar 15 ga watan Disamban shekara 2013 ne, rikici ya barke a tsakanin dakarun da ke goyon bayan wadannan jagorori biyu,lamarin da ya tilasta wa mutane sama da 870,000 kaura daga gidajensu kana da dama suka tsunduma cikin mawuyacin hali na neman agaji.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China