in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Fadan da ake yi a kasar Sudan ta kudu na ci gaba da tilastawa mutane gujewa daga muhallansu
2014-03-14 11:05:13 cri
Ofishin Majalisar dinkin duniya mai gudanar da harkokin samar da agaji ya ce arangamar da ake ci gaba da yi a jihohin Jonglei, Unity da Upper Nile dake kasar Sudan ta kudu yana matsawa mutane ficewa daga gidajensu a inda hakan ya sa ana samun matsala wajen samar da kayan agaji ga masu bukata.

Kakakin Majalisai dinkin duniya Stephane Dujarric ya fada a jiya Alhamis cewar, abokanan aikinsu wadanda ke kokarin samar da kayayyakin agaji na ci gaba da yin yarjejeniya da dukanin bangarorin domin samar da kayayyakin agaji, tare da kwato kaddarorin da aka yi kokarin tabbatar da tsaron lafiyar masu ba da kayayyakin agaji na cikin gidan kasar Sudan ta kudu da na kasashen ketare.

Kakakin na majalisar dinkin duniyar wanda ya yi jawabi a yayin wani taron manema labarai, bai bayar da karin bayani ba a game da yawan adadin mutanen da fadan ya tilasta masu ficewa daga muhallansu.

Jihar Jonglei na daya daga cikin jihohi goma a kasar Sudan ta kudu, kuma ita ce jiha mafi girma da yawan jama'a a jaririyar kasar. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China