in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Uganda za ta janye sojojinta daga Sudan ta Kudu, in ji Wamala
2014-03-15 16:11:33 cri
Babban hafsan sojojin kasar Uganda Janar Katumba Wamala, ya ce kasar sa za ta janye dakarunta daga kasar Sudan ta Kudu, da zarar sojojin kiyaye zaman lafiya na hadin gwiwar yankin sun fara isa kasar.

Janar Wamala wanda ya bayyana wa manema labaru hakan a gundumar Jinja ta Gabashin kasar Uganada a ranar Jumma'a, ya kara da cewa kasarsa ba ta fatan fara janye dakarunta kafin hakan, domin gudun barin kasar Sudan ta Kudun cikin mawuyacin halin rashin tsaro.

Wannan dai tsokaci na Wamala na zuwa ne biyowa bayan matsin lambar da gamayyar kasashen duniya ke wa Uganda kan ta janye sojojinta daga kasar, matakin da kasashen ke cewa zai taimakawa shirin da ake yi na girke dakarun hadin gwiwa.

A yayin taron da shuwagabannin yankin Gabashin nahiyar Afirka suka gudanar a ranar Alhamis ne dai aka yanke shawarar tura tawagar wanzar da zaman lafiyar hadin gwiwa ta PDF zuwa Sudan ta Kudu.

Tun dai cikin watan Disambar bara ne dai Uganda ta jibge rukunin farko na dakarun sojinta a kasar Sudan ta Kudu, matakin da ta ce ta dauka domin kare faruwar kisan kiyashi a kasar. Inda daga bisani kuma ta kara yawan sojin nata bisa bukatar gwamnatin kasar ta kasar Sudan ta Kudu. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China