in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An sace wasu mata a Najeriya
2014-06-24 20:18:48 cri
A makon da ya gabata ne mayakan Boko Haram suka yi awon gaba da mata da wasu 'yan mata yayin da suka kai wasu hare-hare a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya.

Wata majiya ta bayyana cewa, a kalla mutane 30 aka kashe a hare-hare daban-daban da mayakan suka kai a kan kauyuka 4 da ke karamar hukumar Damboa a jihar Borno da ke fama da tashin hankali,yayin da a kalla mata da 'yan mata 60 suka bace sakamakon hare-haren mayakan.

Wani malamin addinin Islama mai suna Aminu Mustapha wanda ya gudu zuwa garin Lassa, ya ce tsakanin ranakun Alhamis da Asabar,mazauna kauyukan Gurblagwa,Yafa,Kummabza da Yaza sun shiga wani hali na garari,sakamakon harin da mayakan na Boko Haram suka kaddamar.

Sai dai jami'an tsaro da na jihar ba su yi karin bayani ba game da lamarin.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China